Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 21:13-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Wannan zai zama muku hanyar ba da shaida.

14. Saboda haka, sai ku ƙudura a ranku, a kan ba za ku damu da yadda za ku mai da jawabi ba.

15. Domin ni ne zan ba ku ikon hurci, da kuma hikima wadda duk abokan adawarku, ba za su iya shanyewa ko musawa ba.

16. Ko da iyayenku ma da 'yan'uwanku, da danginku, da abokanku, sai sun bāshe ku, su kuma sa a kashe waɗansunku.

17. Kowa kuma zai ƙi ku saboda sunana.

18. Amma ba gashin kanku ko ɗaya da zai yi ciwo.

19. Jurewarku ce za ta fisshe ku.”

20. “Sa'ad da kuka ga rundunonin yaƙi sun kewaye Urushalima, sa'an nan ku tabbata ana kusan ribɗe ta.

21. Sa'an nan waɗanda suke a ƙasar Yahudiya, su gudu su shiga duwatsu, na birni su fice, na ƙauye kuma kada su shiga birni.

22. Saboda lokacin sakamako ne, don a cika duk abin da yake rubuce.

23. Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci! Don matsanancin ƙunci zai saukar wa ƙasar, da kuma fushin Allah ga jama'an nan.

24. Za a kashe waɗansu da kaifin takobi, a kuma kakkama waɗansu a kai su bauta zuwa ƙasashen al'ummai duka. Al'ummai kuma za su tattake Urushalima, har ya zuwa cikar zamaninsu.”

Karanta cikakken babi Luk 21