Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 20:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Sai suka jefa shi a bayan shinge, suka kashe shi. To, me ubangijin garkan nan zai yi da su?

16. Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.” Da suka ji haka, suka ce, “Allah ya sawwaƙe!”

17. Amma ya dube su, ya ce, “Wannan da yake a rubuce fa cewa,‘Dutsen da magina suka ƙi,Shi ne ya zama mafificin dutsen gini?’

18. Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje, amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”

19. Nan take malaman Attaura da manyan firistoci suka nema su kama Yesu, don sun lura a kansu ne ya ba da misalin, amma suna jin tsoron jama'a.

20. Sai suka yi ta haƙwansa, suka aiki 'yan rahoto, su kuwa suka nuna kamar su masu adalci ne, da nufin su kama shi a maganarsa, su kuma ba da shi ga mai mulki ya hukunta shi.

Karanta cikakken babi Luk 20