Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:16-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Zai kuma juyo da Isra'ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu.

17. Zai riga shi gaba cikin ruhu da iko irin na Iliya.Yă mai da hankalin iyaye a kan 'ya'yansu,Yă kuma juyo da marasa biyayya su bi hikimar adalai,Ya tanada wa Ubangiji jama'a, ya same su a shirye.”

18. Sai Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta ƙaƙa zan san haka? Ga ni tsoho, maiɗakina kuma ta kwana biyu.”

19. Sai mala'ikan ya amsa ya ce, “Ni ne Jibra'ilu da yake tsaye a gaban Allah. An aiko ni ne in yi maka magana, in kuma yi maka wannan albishir.

20. To, ga shi, za ka bebance, ba za ka iya magana ba, sai a ran da al'amuran nan suka auku, don ba ka gaskata maganata ba, za a kuwa cika ta a lokacinta.”

21. Jama'a suna ta jiran Zakariya, suna mamakin jinkirinsa a Haikali.

22. Da ya fito, ya kāsa yi musu magana. Sai suka gane lalle an yi masa wahayi ne a Haikalin. Sai ya riƙa yi musu nuni, amma ba ya magana.

Karanta cikakken babi Luk 1