Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 5:38-42 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. To, yanzu ma, ina gaya muku, ku fita sha'anin mutanen nan, ku ƙyale su. Idan dai niyyarsu ko aikinsu na mutum ne, ai, zai rushe,

39. amma in na Allah ne, ba dama ku rushe su. Kada fa a same ku kuna gāba da Allah.”

40. Sai suka bi shawara tasa, suka kuma kirawo manzannin, suka yi musu dūka, suka kwaɓe su kada su ƙara magana da sunan Yesu, sa'an nan suka sake su.

41. To, suka tashi daga gaban majalisar, suna farin ciki a kan an ga sun isa su sha wulakanci saboda sunan Yesu.

42. Kowace rana kuwa, ko a Haikali ko a gida, ba su daina koyarwa da yin bishara, cewa Yesu shi ne Almasihu ba.

Karanta cikakken babi A.m. 5