Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 20:8-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Akwai kuwa fitilu da yawa a benen da muka taru.

9. Da wani saurayi a zaune a kan taga, mai suna Aftikos, sai barci ya ci ƙarfinsa sa'ad da Bulus yake ta tsawaita jawabi, da barci mai nauyi ya kwashe shi, sai ya faɗo daga can hawa na uku, aka ɗauke shi matacce.

10. Amma Bulus ya sauka ƙasa, ya miƙe a kansa, ya rungume shi, ya ce, “Kada ku damu, ai, yana da rai.”

11. Da Bulus ya koma sama, ya gutsuttsura gurasa ya ci, ya daɗe yana magana da su, har gari ya waye, sa'an nan ya tashi.

12. Sai suka tafi da saurayin nan a raye, daɗin da suka ji kuwa ba kaɗan ba ne.

13. Mu kuwa muka yi gaba zuwa jirgin, muka miƙe sai Asus da nufin ɗaukar Bulus daga can, don dā ma haka ya shirya, shi kuwa ya yi niyyar bi ta ƙasa.

14. Da ya same mu a Asus, muka ɗauke shi a jirgin, muka zo Mitilini.

15. Daga nan kuma muna tafe a jirgin ruwan dai, kashegari kuma sai ga mu daura da tsibirin Kiyos. Kashegari kuma, ga mu a tsibirin Samas, kashegari kuma sai Militas.

Karanta cikakken babi A.m. 20