Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 20:5-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. waɗanda suka riga tafiya suka jira mu a Taruwasa.

6. Mu kuwa muka tashi daga Filibi a jirgin ruwa, bayan idin abinci marar yisti, muka iske su a Taruwasa bayan kwana biyar. Nan muka zauna har kwana bakwai.

7. A ranar farko ta mako kuma, da muka taru don gutsuttsura gurasa, Bulus ya yi masu jawabi, don ya yi niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta jan jawabin nasa har tsakar dare.

8. Akwai kuwa fitilu da yawa a benen da muka taru.

Karanta cikakken babi A.m. 20