Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 19:20-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Sai kuma Maganar Ubangiji ta ƙara haɓaka, ta kuma fifita ƙwarai.

21. Bayan waɗannan al'amura Bulus ya ƙudura a ransa, cewa in ya zazzaga ƙasar Makidoniya da ta Akaya, za shi Urushalima, ya kuma ce, “Bayan na je can, lalle ne kuma in je in ga birnin Roma.”

22. Da ya aiki mataimakansa biyu Makidoniya, wato Timoti da Arastas, shi kuwa ya ɗan dakata a ƙasar Asiya.

23. A lokacin nan kuwa ba ƙaramin hargitsi aka yi game da wannan hanya ba.

Karanta cikakken babi A.m. 19