Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tim 2:22-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Don haka, sai ka guje wa mugayen sha'awace-sha'awacen ƙuruciya, ka dimanci aikin adalci, da bangaskiya, da ƙauna, da kuma salama, tare da waɗanda suke roƙon Ubangiji da zuciya tsarkakakkiya.

23. Ka ƙi gardandamin banza marasa ma'ana, ka san lalle suna jawo husuma.

24. Bawan Ubangiji kuwa lalle ba zai zama mai husuma ba, sai dai ya zama salihi ga kowa, gwanin koyarwa, mai haƙuri,

25. mai sa abokan hamayyarsa a kan hanya da tawali'u, ko Allah zai sa su tuba, su kai ga sanin gaskiya,

26. su kuɓuce wa tarkon Iblis, su bi nufin Allah, bayan da Iblis ya tsare su.

Karanta cikakken babi 2 Tim 2