Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tas 2:2-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Amma ko da yake dā ma can mun sha wuya, an kuma wulakanta mu a Filibi, kamar yadda kuka sani, duk da haka da taimakon Allahnmu muka sanar da ku bisharar Allah gabagaɗi, amma sai da matsanancin fama.

3. Ai, gargaɗin da muke yi muku babu bauɗewa ko munafunci a ciki, balle yaudara,

4. sai dai kamar yadda Allah ya yarda da mu, ya damƙa mana amanar bishara, haka muke sanar da ita, ba domin mu faranta wa mutane rai ba, sai dai domin mu faranta wa Allah, shi da yake jarraba zukatanmu.

5. Yadda kuka sani, ba mu taɓa yin daɗin baki ko kwaɗayi ba. Allah kuwa shi ne shaida.

Karanta cikakken babi 1 Tas 2