Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 16:5-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Zan zo gare ku bayan na zazzaga ƙasar Makidoniya, don kuwa ta Makidoniya zan bi.

6. Watakila zan jima a wurinku, ko ma in ci damina, don ku yi mini rakiya duk in da za ni.

7. Ba sona ne in gan ku a yanzu in wuce kawai ba, a'a, ina sa zuciya ma in yi kwanaki a wurinku, in Ubangiji ya yarda.

8. Amma zan dakata a Afisa har ranar Fentikos.

9. Don kuwa, an buɗe mini wata hanya mai fāɗi ta yin aiki mai amfani, akwai kuma magabta da yawa.

10. In Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa a cikinku, domin aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi.

11. Kada fa kowa yă raina shi. Ku raka shi lafiya, ya komo a gare ni, domin ina duban hanyarsa tare da 'yan'uwa.

12. Ga zancen ɗan'uwanmu Afolos kuwa, na roƙe shi ƙwarai, don yă zo wurinku, tare da saurar 'yan'uwa, amma ko kusa bai yi nufin zuwa a yanzu ba. Zai zo dai sa'ad da ya ga ya dace.

13. Ku zauna a faɗake, ku dāge ga bangaskiyarku, ku yi ƙwazo, ku yi ƙarfi.

14. Duk abin da za ku yi, ku yi shi da ƙauna.

15. To, 'yan'uwa, kun sani fa jama'ar gidan Istifanas su ne nunan fari a ƙasar Akaya, sun kuwa ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima.

16. Ina roƙonku ku yi wa irin waɗannan mutane biyayya, har ma ga duk waɗanda suke abokan aikinmu da wahalarmu.

17. Na yi farin ciki da zuwan Istifanas, da Fartunatas, da Akaikas, domin sun ɗebe mini kewarku.

18. Sun dai wartsakar da ni da kuma ku. Sai ku kula da irin waɗannan mutane.

Karanta cikakken babi 1 Kor 16