Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 14:8-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. In ba a busa ƙaho sosai ba, wa zai yi shirin yaƙi?

9. Haka ma yake a gare ku. In kun yi magana da wani harshe, wanda ba a fahimta ba, yaya wani zai san abin da ake faɗa? Kun yi magana a banza ke nan!

10. Hakika akwai harsuna iri iri a duniya, ba kuwa wanda ba shi da ma'ana.

11. In kuwa ba na jin harshen, sai in zama bare ga mai maganar, mai maganar kuma ya zama bare a gare ni.

12. Haka ma yake a gare ku. Tun da yake kun ɗokanta da samun bayebaye na Ruhu, sai ku himmantu ku ba da ƙarfinku ga inganta ikkilisiya.

13. Saboda haka duk mai magana da wani harshe, sai yă yi addu'a a yi masa baiwar fassara.

14. In na yi addu'a da wani harshe, ruhuna ne yake addu'a, amma tunanina bai amfana kowa ba.

15. To, ƙaƙa ke nan? Zan yi addu'a da ruhuna, zan kuma yi a game da tunanina. Zan yi waƙar yabon Allah da ruhuna, zan yi a game da tunanina.

16. In ba haka ba, in ka gode wa Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda yake jahili zai ce, “Amin,” a kan godiyar da kake yi, in bai san abin da kake faɗa ba?

17. Ko da yake ka gode wa Allah sosai, ai, ɗan'uwanka bai ƙaru da kome ba.

Karanta cikakken babi 1 Kor 14