Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 8:2-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. “Ni Ubangiji Mai Runduna ina kishin Sihiyona ƙwarai.

3. Zan koma wurin Sihiyona, in zauna a tsakiyar Urushalima. Za a ce da Urushalima birnin gaskiya, da kuma dutsen Ubangiji Mai Runduna, tsattsarkan dutse.

4. Tsofaffi, mata, da maza, za su zauna a titunan Urushalima, kowa yana tokare da sanda saboda tsufa.

5. Samari da 'yan mata zan sa su cika titunan Urushalima, suna wasa.

Karanta cikakken babi Zak 8