2. “Ni Ubangiji Mai Runduna ina kishin Sihiyona ƙwarai.
3. Zan koma wurin Sihiyona, in zauna a tsakiyar Urushalima. Za a ce da Urushalima birnin gaskiya, da kuma dutsen Ubangiji Mai Runduna, tsattsarkan dutse.
4. Tsofaffi, mata, da maza, za su zauna a titunan Urushalima, kowa yana tokare da sanda saboda tsufa.
5. Samari da 'yan mata zan sa su cika titunan Urushalima, suna wasa.