Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 8:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Haka kuma na ƙudura a waɗannan kwanaki in yi wa Urushalima da jama'ar Yahuza alheri. Kada ku ji tsoro!

16. Abubuwan da za ku yi ke nan, ku faɗa wa juna gaskiya, ku yi shari'a ta gaskiya a majalisunku, domin zaman lafiya.

17. Kada ku ƙulla wa junanku sharri, kada kuma ku so yin rantsuwa ta ƙarya, gama ina ƙin waɗannan abubuwa duka, ni Ubangiji na faɗa.”

18. Ubangiji Mai Runduna ya yi magana da ni, ya ce,

19. “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, azumi na watan huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai, da na watan goma, za su zama lokatan murna, da farin ciki, da idodin farin ciki, ga jama'ar Yahuza, saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama.

20. “Mutanen birane da yawa za su hallara.

Karanta cikakken babi Zak 8