Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 6:8-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ya kuma kira ni, ya ce, “Duba, waɗanda suka tafi ƙasar arewa sun sa fushin Ubangiji ya huce.”

9. Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

10. “Ka karɓi sadaka daga Heldai, da Tobiya, da Yedaiya waɗanda suka komo daga bautar talala a Babila. A ranar kuma ka tafi gidan Yosiya ɗan Zafaniya.

11. Ka karɓi azurfa da zinariya a wurinsu, ka ƙera kambi, ka sa shi a kan Yoshuwa, ɗan Yehozadak, babban firist.

12. Ka kuwa ce masa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, mutumin da sunansa Reshe, zai yi girma a inda yake, zai kuma gina Haikalin Ubangiji.

13. Shi ne zai gina Haikalin Ubangiji, ya kuma sami girma, ya yi mulki kamar sarki, ya kuma zama firist. Kome kuwa zai tafi daidai.’

Karanta cikakken babi Zak 6