Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 6:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Na kuma ɗaga idona, sai na ga karusa huɗu suna fitowa daga tsakanin duwatsu biyu. Duwatsun kuwa na tagulla ne.

2. Dawakai aharasai ne suke jan karusa ta fari, ta biyu kuwa akawalai ne suke janta.

3. Na uku kuma dawakai kiliyai ne suke janta, ta huɗu kuwa hurdu ne yake janta.

4. Sa'an nan na ce wa mala'ikan da yake magana da ni, “Mene ne waɗannan, ya ubangijina?”

Karanta cikakken babi Zak 6