Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zak 14:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ga ranar Ubangiji tana zuwa sa'ad da za a raba ganimar da aka ƙwace daga gare ku a kan idonku.

2. Gama zan tattara dukan al'ummai su yi yaƙi da Urushalima. Za a ci birnin, a washe gidajen. Za a yi wa mata faɗe. Za a kai rabin mutanen birnin bauta, amma za a bar sauran mutanen a cikin birnin.

3. Sa'an nan Ubangiji zai tafi ya yi yaƙi da waɗannan al'ummai kamar yadda ya yi a dā.

4. A wannan rana ƙafafunsa za su tsaya a bisa Dutsen Zaitun wanda yake wajen gabas da Urushalima. Dutsen Zaitun zai tsage biyu daga gabas zuwa yamma, ya zama babban kwari. Sashi guda na dutsen zai janye zuwa wajen kudu. Ɗaya sashin kuma zai janye zuwa wajen arewa.

Karanta cikakken babi Zak 14