Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 94:7-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Suna cewa, “Ai, Ubangiji ba ya ganinmu,Allah na Isra'ila ba ya lura da abin da yake faruwa!”

8. Ya jama'ata, ƙaƙa kuka zama dakikai, wawaye haka?Sai yaushe za ku koya?

9. Allah ya yi mana kunnuwa, shi ba zai ji ba?Allah ya yi mana idanu, shi ba zai gani ba?

10. Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba?Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne?

11. Ubangiji ya san tunaninsu,Ya san kuma hujjojinsu na rashin hankali.

12. Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa,Mutumin da kake koya masa shari'arka.

13. Don ka ba shi hutawa a kwanakin wahala,Kafin a haƙa wa mugaye kabari.

14. Ubangiji ba zai rabu da jama'arsa ba,Ba zai rabu da waɗanda suke nasa ba.

15. Adalci kuma zai sāke dawowa cikin majalisun alƙalai,Dukan adalai kuwa za su yi na'am da shi.

16. Wa zai tsaya mini gāba da mugaye?Wa zai goyi bayana gāba da masu aikata mugunta?

17. Da ba domin Ubangiji ya taimake ni ba,Ai, da tuni na kai ƙasar da ba a motsi.

18. Na ce, “Ina kan fāɗuwa,”Amma, ya Ubangiji, madawwamiyar ƙaunarka ta riƙe ni.

19. Sa'ad da nake alhini, ina cikin damuwa,Ka ta'azantar da ni, ka sa in yi murna.

Karanta cikakken babi Zab 94