Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 83:6-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Su ne mutanen Edom, da Isma'ilawa,Da mutanen Mowab, da Hagarawa,

7. Da mutanen Gebal, da na Ammon, da na Amalek,Da na Filistiya, da na Taya.

8. Assuriya ma ta haɗa kai da su,Haɗa kai ke nan mai ƙarfi da zuriyar Lutu.

9. Ka yi musu yadda ka yi wa Madayanawa,Ka yi musu yadda ka yi wa SiseraDa Yabin a Kogin Kishon,

10. Waɗanda aka kora a Endor,Gawawwakinsu kuwa suka ruɓe a ƙasa.

11. Ka yi wa shugabannin yaƙinsu yadda ka yi wa Oreb da Ziyib,Ka kori dukan masu mulkinsu yadda ka kori Zeba da Zalmunna,

12. Waɗanda suka ce, “Za mu ƙwace ƙasar da take ta Allah, ta zama tamu.”

13. Ya Allahna, ka warwatsa su kamar ƙura,Ka warwatsa su kamar ciyayin da iska take hurawa.

Karanta cikakken babi Zab 83