Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 80:1-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ka kasa kunne gare mu, ya Makiyayin Isra'ila,Ka ji mu, kai da kake shugaban garkenka,Da kake zaune a kan kursiyinka, a bisa kerubobi.

2. Ka bayyana ƙaunarka ga kabilar Ifraimu,Da ta Biliyaminu, da ta Manassa!Ka nuna mana ikonka,Ka zo ka cece mu!

3. Ka komo da mu, ya Allah!Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

4. Har yaushe ke nan ya Ubangiji Allah Mai Runduna,Za ka yi ta fushi da addu'o'in jama'arka?

5. Ka ciyar da mu da hawaye,Ka shayar da mu da babban ƙoƙo na hawaye.

6. Ka bar al'umman da take makwabtaka da muSu yi ta faɗa a kan ƙasarmu,Abokan gābanmu kuma suna yi mana ba'a.

7. Ka komo da mu, ya Allah Mai Runduna!Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

8. Ka fito da kurangar inabi daga cikin Masar,Ka kori sauran al'umma,Ka dasa kurangar a ƙasarsu.

9. Ka gyara mata wuri don ta yi girma,Saiwoyinta suka shiga ƙasa sosai,Ta yaɗu, ta rufe dukan ƙasar.

10. Ta rufe tuddai da inuwarta,Ta rufe manya manyan itatuwan al'ul da rassanta.

11. Rassanta sun miƙe har Bahar Rum,Har zuwa Kogin Yufiretis.

Karanta cikakken babi Zab 80