13. Da ƙarfin ikonka ka raba teku,Ka farfashe kawunan dodannin ruwa,
14. Ka ragargaje kawunan kadduna,Ka kuwa ba mutanen hamada su ci.
15. Ka sa ruwan maɓuɓɓugai ya yi gudu,Ka sa manyan koguna su ƙafe.
16. Ka halicci yini da dare,Ka sa rana da wata a wurarensu.
17. Ka yi wa duniya kan iyaka,Ka kuwa yi lokatan damuna da na rani.