Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 74:11-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Me ya sa ka ƙi taimakonmu?Ka tasar musu ka hallaka su!

12. Amma ya Allah, kai ne Sarkinmu tun daga farko,Ka yi nasara da duniya.

13. Da ƙarfin ikonka ka raba teku,Ka farfashe kawunan dodannin ruwa,

14. Ka ragargaje kawunan kadduna,Ka kuwa ba mutanen hamada su ci.

15. Ka sa ruwan maɓuɓɓugai ya yi gudu,Ka sa manyan koguna su ƙafe.

16. Ka halicci yini da dare,Ka sa rana da wata a wurarensu.

17. Ka yi wa duniya kan iyaka,Ka kuwa yi lokatan damuna da na rani.

18. Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba'a,Su wawaye ne waɗanda suke raina ka.

Karanta cikakken babi Zab 74