Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 73:9-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Sukan faɗi baƙar magana a kan Allah na Sama,Su ba da umarnai na girmankai ga mutane a duniya,

10. Har jama'ar Allah ma sukan koma wurinsu,Suna ɗokin gaskata dukan abin da suke faɗa musu.

11. Sukan ce, “Ai, Allah ba zai sani ba,Maɗaukaki ba zai bincika ba!”

12. Haka mugaye suke.Suna da dukiya da yawa, amma sai ƙaruwa suke ta yi.

13. Ashe, a banza nake kiyaye kaina da tsarki,Hannuwana kuma a tsabtace daga zunubi?

14. Ya Allah, ka sa ina shan wahala dukan yini,Kana horona kowace safiya!

15. Da na faɗi waɗannan abubuwa,Da na zama marar gaskiya ga jama'arka.

16. Don haka na yi iyakar ƙoƙari in fahimci wannan,Ko da yake ya cika wuya,

17. Sai sa'ad da na shiga Haikalinka,Sa'an nan na fahimci abin da zai sami mugaye.

18. Hakika ka sa su a wurare masu santsi,Ka sa su su fāɗi su hallaka sarai!

19. Cikin ƙyaftawar ido aka hallaka su,Suka yi mummunan ƙarshe!

20. Ya Ubangiji, kamar mafarki sukeWanda akan manta da shi da safe,Sa'ad da mutum ya farka yakan manta da kamanninsa.

21. Sa'ad da zuciyata ta ɓaci,Hankalina ya tashi,

Karanta cikakken babi Zab 73