11. Sukan ce, “Ai, Allah ba zai sani ba,Maɗaukaki ba zai bincika ba!”
12. Haka mugaye suke.Suna da dukiya da yawa, amma sai ƙaruwa suke ta yi.
13. Ashe, a banza nake kiyaye kaina da tsarki,Hannuwana kuma a tsabtace daga zunubi?
14. Ya Allah, ka sa ina shan wahala dukan yini,Kana horona kowace safiya!
15. Da na faɗi waɗannan abubuwa,Da na zama marar gaskiya ga jama'arka.
16. Don haka na yi iyakar ƙoƙari in fahimci wannan,Ko da yake ya cika wuya,