Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 72:1-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ka koya wa sarki ya yi shari'aDa adalcinka, ya Allah,Ka kuma ba shi shari'arka,

2. Don ya yi mulkin jama'arka bisa kan shari'a,Ya kuma bi da mulki da adalci.

3. Ka sa ƙasar ta mori wadatarta,Ka sa al'ummar ta san adalci.

4. Ka sa sarki ya yi wa talakawa shari'ar gaskiya,Ya taimaki waɗanda suke da bukata,Ya kuma hukunta azzalumai!

5. Ka sa su girmama kaMuddin rana tana haskakawa,Muddin wata yana ba da haske dukan lokaci.

6. Ka sa sarki ya zama kamar ruwan sama a gonaki,Ya zama kamar yayyafi a bisa ƙasa.

7. Ka sa adalci ya bunƙasa a zamaninsa,Wadata ta dawwama muddin wata na haskakawa.

8. Mulkinsa ya kai daga teku zuwa teku,Daga Kogin Yufiretis, har zuwa iyakar duniya.

9. Kabilan hamada za su durƙusa a gabansa,Abokan gābansa za su kwanta warwar a cikin ƙura.

10. Sarakunan Esbanya da na tsibirai,Za su ba shi kyautai,Sarakunan Arabiya da na HabashaZa su kawo masa kyautai.

11. Dukan sarakuna za su durƙusa a gabansa,Dukan sauran al'umma za su bauta masa!

12. Yakan ceci matalauta waɗanda suka yi kira gare shi,Da waɗanda suke da bukata,Da waɗanda ba a kula da su.

13. Yakan ji tausayin gajiyayyu da matalauta,Yakan ceci rayukan waɗanda suke da bukata.

Karanta cikakken babi Zab 72