10. Ka jarraba mu, ya Allah,Kamar yadda ake tace azurfa da wuta,Haka nan ka jarraba mu.
11. Ka bar mu muka fāɗa a tarko,Ka ɗora mana kaya masu nauyi.
12. Ka bar maƙiyanmu suka tattaka mu,Mun ratsa ta cikin wuta da rigyawa,Amma yanzu ka kawo mu a lafiyayyen wuri.
13. Zan kawo hadayun ƙonawa a ɗakinka,Zan miƙa maka abin da na alkawarta.
14. Zan ba ka abin da na ce zan bayar,A lokacin da nake shan wahala.