13. Da fushinka ka hallaka su,Ka hallaka su ɗungum.Sa'an nan jama'a za su sani Allah yana mulkin Isra'ila,Mulkinsa ya kai ko'ina a duniya!
14. Da maraice maƙiyana suka komo,Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni.
15. Suna kai da kawowa ko'ina neman abinci,In ba su sami abin da ya ishe su ba,Sukan yi gunaguni.
16. Amma zan raira waƙa a kan ikonka,Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfiGa zancen madawwamiyar ƙaunarka.Kai mafaka ne a gare ni,Wurin ɓuya a kwanakin wahala.
17. Zan yabe ka, mai tsarona,Allah ne mafakata,Allah wanda ya ƙaunace ni.