Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 59:11-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Kada ka kashe su, ya Allah, don kada jama'ata su manta.Ka watsar da su da ikonka, ka hallaka su ya Ubangiji mai kiyaye mu!

12. Zunubi na cikin leɓunansu, maganganunsu na zunubi ne,Da ma a kama su saboda girmankansu,Domin suna la'antarwa, suna ƙarya!

13. Da fushinka ka hallaka su,Ka hallaka su ɗungum.Sa'an nan jama'a za su sani Allah yana mulkin Isra'ila,Mulkinsa ya kai ko'ina a duniya!

14. Da maraice maƙiyana suka komo,Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni.

15. Suna kai da kawowa ko'ina neman abinci,In ba su sami abin da ya ishe su ba,Sukan yi gunaguni.

16. Amma zan raira waƙa a kan ikonka,Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfiGa zancen madawwamiyar ƙaunarka.Kai mafaka ne a gare ni,Wurin ɓuya a kwanakin wahala.

17. Zan yabe ka, mai tsarona,Allah ne mafakata,Allah wanda ya ƙaunace ni.

Karanta cikakken babi Zab 59