Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 50:7-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. “Ku ji, ya ku jama'ata, zan kuwa yi magana,Zan ba da shaida gāba da ku, ya Isra'ila.Ni ne Allah, Allahnku.

8. Ban tsauta muku saboda hadayunku ba,Ko saboda hadayu na ƙonawa da kuke ta miƙa mini kullum.

9. Ba na bukatar bijimai daga gonakinku,Ko awaki daga garkunanku.

10. Gama namomin jeji nawa ne,Dubban shanu da suke kan tuddai kuma nawa ne.

11. Dukan tsuntsayen da suke tashi a sararin sama nawa ne,Da dukan masu rai da suke ƙasa.

12. “Da ina jin yunwa ba sai na faɗa muku ba,Gama da duniya da dukan abin da yake cikinta nawa ne.

Karanta cikakken babi Zab 50