Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 50:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Allah Maɗaukaki, Ubangiji, ya yi magana,Yana kiran dukan duniya, daga gabas zuwa yamma.

2. Allah yana haskakawa daga Sihiyona,Da cikar jamalin Sihiyona.

3. Allahnmu ya zo, ba a ɓoye yake ba,Wuta mai cinyewa na tafe a gabansa,Babban hadiri kuwa na kewaye da shi.

4. Ya kira sammai da duniya su zama shaidu,Su ga yadda yake shara'anta jama'arsa.

5. Ya ce, “Ku tattaro mini amintattuna,Waɗanda suka cika alkawarin da yake tsakanina da su,Ta wurin miƙa hadaya.”

Karanta cikakken babi Zab 50