1. Allah Maɗaukaki, Ubangiji, ya yi magana,Yana kiran dukan duniya, daga gabas zuwa yamma.
2. Allah yana haskakawa daga Sihiyona,Da cikar jamalin Sihiyona.
3. Allahnmu ya zo, ba a ɓoye yake ba,Wuta mai cinyewa na tafe a gabansa,Babban hadiri kuwa na kewaye da shi.
4. Ya kira sammai da duniya su zama shaidu,Su ga yadda yake shara'anta jama'arsa.