Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 38:16-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Kada ka bar magabtana su yi murna saboda wahalata.Kada ka bar su su yi kirari a kan faɗuwata!

17. Ina gab da fāɗuwa,Ina cikin azaba kullum.

18. Na hurta zunubaina,Sun cika ni da taraddadi.

19. Magabtana lafiyayyu ne masu ƙarfi.Waɗanda yake ƙina ba dalili, suna da yawa.

20. Masu rama nagarta da mugunta,Suna gāba da ni,Domin ina ƙoƙarin aikata abin da yake daidai.

21. Kada ka yashe ni, ya Ubangiji,Kada ka rabu da ni, ya Allahna!

22. Sai ka taimake ni yanzu, ya Ubangiji, Mai Cetona!

Karanta cikakken babi Zab 38