Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 22:4-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Kakanninmu suka dogara gare ka,Sun dogara gare ka, ka kuwa cece su.

5. Suka yi kira gare ka, suka tsira daga hatsari,Suka dogara gare ka, ba su kuwa kunyata ba.

6. A yanzu dai ni ba mutum ba ne, tsutsa ne kawai,Rainanne, abin ba'a ga kowa da kowa!

7. Duk wanda ya gan niSai yă maishe ni abin dariya,Suna zunɗena da harshensu suna kaɗa kai.

8. Suka ce, “Ka dogara ga Ubangiji,Me ya sa bai cece ka ba?Idan Ubangiji na sonka,Don me bai taimake ka ba?”

9. Kai ne ka fito da ni lafiya a lokacin da aka haife ni,A lokacin da nake jariri ka kiyaye ni.

10. Tun daga lokacin da aka haife ni nake dogara gare ka,Kai ne Allahna tun daga ran da aka haife ni.

11. Kada ka yi nisa da ni!Wahala ta gabato,Ba kuwa mai taimako.

12. Magabta da yawa sun kewaye ni kamar bijimai,Dukansu suna kewaye da ni,Kamar bijimai masu faɗa na ƙasar Bashan.

13. Sun buɗe bakinsu kamar zakoki,Suna ruri, suna ta bina a guje.

14. Ƙarfina ya ƙare,Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa.Dukan gaɓoɓina sun guggulle,Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.

15. Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura,Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama.Ka bar ni matacce cikin ƙura.

16. Ƙungiyar mugaye na kewaye da ni,Suka taso mini kamar garken karnuka,Suka soke hannuwana da ƙafafuna.

17. Ana iya ganin ƙasusuwana duka.Magabtana suka dube ni, suka zura mini ido.

Karanta cikakken babi Zab 22