Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 2:3-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Suna cewa, “Bari mu 'yantar da kanmu daga mulkinsu,Bari mu fice daga ƙarƙashinsu!”

4. Ubangiji ya yi dariya daga kan kursiyinsa can Sama,Ya mai da su abin dariya.

5. Ya yi musu magana da fushi,Ya razanar da su da hasalarsa,

6. Ya ce, “A bisa Sihiyona, dutsena tsattsarka,Na naɗa sarkina.”

7. Sarkin ya ce, “Zan yi shelar abin da Ubangiji ya hurta.Ubangiji ya ce mini, ‘Kai ɗana ne,Yau ne na zama mahaifinka.

8. Ka yi roƙo, zan kuwa ba ka dukan al'ummai,Dukan duniya kuma za ta zama taka.

9. Za ka mallake su da sandan ƙarfe,Za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu.’ ”

Karanta cikakken babi Zab 2