Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 135:12-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa,Ya ba da ita ga Isra'ila.

13. Ya Ubangiji, kullayaumi mutane za su sani kai ne Allah,Dukan tsararraki za su tuna da kai.

14. Ubangiji zai ji juyayin mutanensa,Zai 'yantar da bayinsa.

15. Gumakan al'ummai, da azurfa da zinariya aka yi su,Hannuwan mutane ne suka siffata su.

16. Suna da bakuna, amma ba sa magana,Da idanu, amma ba sa gani.

17. Suna da kunnuwa, amma ba sa ji,Ba kuma numfashi a bakinsu.

18. Ka sa su waɗanda suka yi su,Da dukan waɗanda suke dogara gare su,Su zama kamar gumakan da suka yi!

19. Ku yabi Ubangiji, ya jama'ar Isra'ila,Ku yabe shi, ya ku firistocin Allah!

Karanta cikakken babi Zab 135