7. Kada ki yi shakka, ya zuciyata,Gama Ubangiji yana yi mini alheri.
8. Ubangiji ya cece ni daga mutuwa,Ya share hawayena,Bai bari a kāshe ni ba.
9. Don haka nake tafiya a gaban UbangijiA duniyar masu rai.
10. Na dai yi ta gaskatawa, ko da yakeNa ce, “An ragargaza ni sarai.”
11. Sa'ad da na ji tsoro na ce,“Ba wanda za a iya dogara gare shi.”
12. Me zan bayar ga UbangijiSaboda dukan alheransa gare ni?
13. Zan miƙa hadaya ta sha ga Ubangiji,Ina gode masa domin dā ya cece ni.