Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 115:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A gare ka kaɗai, ya Ubangiji,A gare ka kaɗai, ba a gare mu ba,Dole a girmama ka,Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka.

2. Me ya sa sauran al'umma suke tambayarmu,“Ina Allahnku?”

3. Allahnmu yana Sama,Yana aikata yadda yake so.

4. Amma nasu alloli na azurfa da zinariya ne,Da hannu aka siffata su.

5. Suna da baki, amma ba sa magana,Suna da idanu, amma ba sa gani.

6. Suna da kunnuwa, amma ba sa ji,Suna da hanci, amma ba sa jin ƙanshi.

Karanta cikakken babi Zab 115