Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 102:17-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Zai saurari jama'arsa wadda ya rabu da ita,Zai kuwa ji addu'arta.

18. Ku rubuta abin da Ubangiji ya aikata don zamani mai zuwa,Don waɗanda ba a haife su ba tukuna,Su ma su yabe shi.

19. Ubangiji ya duba ƙasaDaga Sama, tsattsarkan wurinsa,Daga Sama ya dubi duniya,

20. Don ya ji nishin ɗaurarru,Don ya saki waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa.

21. Saboda wannan mutane za su yi shelar sunan Ubangiji a Sihiyona,Za su yi masa godiya a Urushalima,

22. Sa'ad da sauran al'umma da mulkoki suka taruDon su yi wa Ubangiji sujada.

23. Tun ina ƙaramin yaro Ubangiji ya sa na rasa ƙarfi,Ya gajerta kwanakina.

24. Ya Allahna, kada ka ɗauke ni a yanzu,Tun da yake ban tsufa ba tukuna!Ya Ubangiji har abada kake.

25. Ka halicci duniya tun tuntuni,Da ikonka ne ka yi sammai.

Karanta cikakken babi Zab 102