Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 9:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ranar hukunci ta zo, ranar ramako ta iso,Isra'ila za ta sani!An ce annabi wawa ne,Mutumin da yake da ruhu kuwa mahaukaci ne,Saboda yawan muguntarku da ƙiyayyarku.

8. Ifraimu mai tsaro ne a gaban Allahna, annabi kuwa,Duk da haka sun zama kamar mai kafa tarkon kama tsuntsu, a farkon kaka.Akwai ƙiyayya a cikin Haikalin Allahnsu.

9. Sun yi zurfi cikin rashin gaskiyaKamar a kwanakin Gibeya,Ubangiji zai tuna da muguntarsu.Zai hukunta su saboda zunubansu.

10. Ubangiji ya ce, “Na iske Isra'ila a jeji kamar inabi,Na ga kakanninku kamar nunan fari na 'ya'yan ɓaure,Amma da suka zo Ba'al-feyor, sai suka keɓe kansu ga Ba'al.Suka zama abin ƙyama kamar abin da suke ƙauna.

11. Darajar Ifraimu za ta tashi kamar tsuntsu,Ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki!

Karanta cikakken babi Yush 9