Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 8:6-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ai, mai aikin hannu ne ya yi shi a Isra'ila!Gunki ne ba Allah ba ne.Za a farfashe siffar maraƙin Samariya.

7. Gama sun shuka iskaDon haka zu su girbe guguwa.Hatsin da yake tsaye ba shi da zangarniya,Ba zai yi tsaba ba.Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci,

8. Isra'ila kamar kowace al'umma ce.Suna cikin al'ummaiKamar kaskon da ba shi da amfani,

9. Gama sun haura zuwa Assuriya,Kamar jakin jeji da yake yawo shi kaɗai.Mutanen Ifraimu sun yi ijara da abokan tsafinsu.

10. Ko da yake sun yi ijara da abokai daga cikin al'ummai,Yanzu zan tattara su, in hukunta su.Sa'an nan za su fara ragowa,Ta wurin tunanin nawayar Sarkin sarakuna.

11. “Da yake Ilfraimu ta yawaita bagadan zunubi,Sun zama mata bagadai na yin zunubi.

Karanta cikakken babi Yush 8