Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 8:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ko da yake sun yi ijara da abokai daga cikin al'ummai,Yanzu zan tattara su, in hukunta su.Sa'an nan za su fara ragowa,Ta wurin tunanin nawayar Sarkin sarakuna.

11. “Da yake Ilfraimu ta yawaita bagadan zunubi,Sun zama mata bagadai na yin zunubi.

12. Ko da na rubuta mata dokokina sau da yawo,Za ta ɗauke su wani baƙon abu ne kawai.

13. Suna jin daɗin miƙa hadayu don cin naman,Amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu.Ubangiji zai tuna da muguntarsu,Zai hukunta su saboda zunubansu.Za su koma Masar.

14. “Gama mutanen Isra'ila sun manta da Mahaliccinsu,Sai sun gina manyan gidaje masu daraja.Mutanen Yahuza kuma sun yawaita biranensu masu garu,Amma ni Ubangiji, zan aika da wuta a kan biranensu,Ta ƙone fādodinsu.”

Karanta cikakken babi Yush 8