1. Ubangiji ya ce, “Ki sa ƙaho a bakinki,Kamar gaggafa, haka maƙiyi ya kawo sura a kan ƙasar Ubangiji,Domin mutanena sun ta da alkawarina,Sun kuma keta dokokina.
2. Sun yi kuka a wurina,Suna cewa, ‘Ya Allah, mu Isra'ila mun san ka!’
3. Isra'ila ta ƙi abin da yake mai kyau,Don haka abokan gāba sun fafare ta.