Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yush 7:5-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. A ranar bikin sarki,Sukan sa sarki da shugabanni su bugu da ruwan inabi.Yakan yi cuɗanya da shakiyai.

6. Zukatansu suna ƙuna da ƙullaƙulle kamar tanderu.Fushinsu na ci dare farai,Da safe fushinsu yana ci bal-bal kamar harshen wuta.

7. “Dukansu suna da zafi kamar tanderu.Suna kashe masu mulkinsu.Dukan sarakunansu sun faɗi.Ba wanda ya kawo mini kuka.”

8. Ubangiji ya ce, “Mutanen Ifraimu sun haɗa kansu da al'ummai,Sun zama kamar wainar da ba a juya ba.

9. Baƙi sun cinye ƙarfinsu, su kuwa ba su sani ba,Furfura ta faso musu, amma ba su sani ba.

10. Girmankan mutanen Isra'ila ya kai ƙararsu,Duk da haka ba wanda ya komo wurin Ubangiji Allahnsu,Ba su kuwa neme shi ba.

11. Ifraimu kamar kurciya take, marar wayo, marar hankali,Takan tafi Masar da Assuriya neman taimako.

12. Lokacin da suke tafiya, zan shimfiɗa musu ragata,Zan saukar da su ƙasa kamar yadda akan yi wa tsuntsun da yake tashi sama.Zan hukunta su saboda mugayen ayyukansu.

13. “Tasu ta ƙare, gama sun ratse, sun rabu da ni.Halaka za ta auka musu domin sun tayar mini.Ko da yake zan cece su, duk da haka suna faɗar karya a kaina.

14. Ba su yi kuka gare ni da zuciya ɗaya ba,Sa'ad da suke kuka a gadajensu,Sun tsattsaga jikinsu domin abinci da ruwan inabi.Sun yi mini tawaye.

15. Ko da yake na horar da su, na ƙarfafa damatsansu,Duk da haka suna shirya mini maƙarƙashiya.

Karanta cikakken babi Yush 7