Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yun 1:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ana nan sai Ubangiji ya yi magana da Yunusa, ɗan Amittai, ya ce,

2. “Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka faɗakar da su, gama na ga irin muguntarsu.”

3. Amma maimakon Yunusa yă tafi, sai ya gudu daga wurin Ubangiji zuwa Tarshish. Ya tafi Yafa, nan ya sami jirgin ruwa yana gab da tashi zuwa Tarshish, ya kuwa biya kuɗinsa, ya shiga tare da masu jirgin zuwa can don yă tsere wa Ubangiji.

4. Amma Ubangiji ya aika da iska mai ƙarfi a tekun, hadirin ya tsananta ƙwarai har jirgin yana bakin farfashewa.

Karanta cikakken babi Yun 1