Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Yun 1 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Yunusa Ya Yi Gudun Ubangiji

1. Ana nan sai Ubangiji ya yi magana da Yunusa, ɗan Amittai, ya ce,

2. “Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka faɗakar da su, gama na ga irin muguntarsu.”

3. Amma maimakon Yunusa yă tafi, sai ya gudu daga wurin Ubangiji zuwa Tarshish. Ya tafi Yafa, nan ya sami jirgin ruwa yana gab da tashi zuwa Tarshish, ya kuwa biya kuɗinsa, ya shiga tare da masu jirgin zuwa can don yă tsere wa Ubangiji.

4. Amma Ubangiji ya aika da iska mai ƙarfi a tekun, hadirin ya tsananta ƙwarai har jirgin yana bakin farfashewa.

5. Dukan matuƙan jirgin suka firgita, sai kowannensu ya shiga roƙon allahnsa. Suka yi ta jefar da kayan da suke cikin jirgin a ruwa don su sami sauƙi. Yunusa kuwa yana can cikin jirgi, a kwance, yana ta sharar barci.

6. Can shugaban jirgin ya iske shi, ya ce masa, “Me ya sa kake barci? Tashi ka roƙi allahnka, watakila allahnka zai ji tausayinmu, yă cece mu.”

7. Matuƙan jirgin kuwa suka ce wa junansu, “To, bari mu jefa kuri'a mu gani ko alhakin wane ne ya jawo mana wannan bala'i da muke ciki.” Sai suka jefa kuri'a, kuri'ar kuwa ta fāɗa a kan Yunusa.

8. Suka ce masa, “Ka faɗa mana, laifin wane ne ya jawo mana wannan masifa? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Daga wace al'umma kake?”

9. Sai Yunusa ya ce, “Ni Ba'ibrane ne, ina bin Ubangiji Allah na Sama, wanda ya yi teku da ƙasa.”

10. Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” Sun sani ya gudu ne daga wurin Ubangiji, gama ya riga ya faɗa musu.

11. Hadirin kuwa sai ƙaruwa yake ta yi. Matuƙan jirgin kuwa suka ce masa, “Me za mu yi maka domin tekun ya lafa?”

12. Yunusa ya ce, “Sai ku ɗauke ni ku jefa ni cikin tekun, sa'an nan hadirin zai lafa. Gama na sani saboda ni ne wannan hadiri mai banrazana ya auko muku.”

13. Matuƙan jirgin kuwa suka yi ta tuƙi da iyakar ƙarfinsu don su kai gaɓa, amma suka kāsa domin hadirin yana ta ƙaruwa.

14. Suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Ya Ubangiji, muna roƙonka kada ka bar mu mu halaka saboda ran mutumin nan, kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka yi abin da ya gamshe ka.”

15. Sai suka ɗauki Yunusa suka jefa shi cikin teku, nan take teku ta lafa.

16. Sai matuƙan jirgin suka ji tsoron Ubangiji ƙwarai, har suka ba da sadaka, suka kuma yi wa'adi ga Ubangiji.

17. Ubangiji kuwa ya umarci wani babban kifi ya haɗiye Yunusa. Yunusa kuwa ya yi yini uku da dare uku a cikin cikin kifin.