Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Neh 5:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai mata da maza suka yi ta kuka ƙwarai saboda 'yan'uwansu Yahudawa.

2. Akwai waɗanda suka ce, “Mu da 'ya'yanmu mata da maza muna da yawa, sai mu sami hatsi don mu ci mu rayu.”

3. Waɗansu kuma suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”

4. Akwai waɗansu kuma da suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.

5. Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne, 'ya'yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duka da haka muna tilasta wa 'ya'yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma waɗansu daga cikin 'ya'yanmu mata an riga an bautar da su, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”

6. Ni Nehemiya na husata ƙwarai, sa'ad da na ji kukansu da wannan magana.

Karanta cikakken babi Neh 5