Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Neh 13:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A wannan rana aka karanta daga littafin Musa a kunnuwan jama'a. A cikinsa aka tarar da inda aka rubuta, cewa kada Ba'ammone, ko mutumin Mowab ya shiga taron jama'ar Allah.

2. Gama ba su taryi jama'ar Isra'ila da abinci da abin sha ba, amma suka yi ijara da Bal'amu ya zo ya la'anta musu su, amma Allahnmu ya juyar da la'anar ta zama albarka.

3. Da mutane suka ji dokokin, sai suka ware dukan waɗanda suke ba Isra'ilawa ba.

4. Kafin wannan lokaci Eliyashib, firist, wanda aka sa shi shugaban ɗakunan ajiya na Haikalin Allahnmu, wanda yake da dangantaka da Tobiya,

Karanta cikakken babi Neh 13