Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mika 7:8-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ya maƙiyina, kada ka yi murna akaina,Gama sa'ad da na fāɗi, zan tashikuma.Sa'ad da na zauna cikin duhu,Ubangiji zai haskaka ni.

9. Zan ɗauka fushin Ubangiji ne,Gama na yi masa zunubi,Sai lokacin da ya ji da'awata,Har ya yanke mini shari'a.Zai kawo ni zuwa wurin haske,Zan kuwa ga cetonsa.

10. Sa'an nan maƙiyina wanda suke ce mini,“Ina Ubangiji Allahnka?”Zai gani, ya kuma ji kunya.Idanuna za su gan shi lokacin da akatattake shiKamar taɓo a titi.

11. Za a faɗaɗa iyakarkaA ranar da za a gina garunka.

12. A waccan rana mutane za su zowurinka,Daga Assuriya har zuwa Masar,Daga Masar zuwa Kogin Yufiretis,Daga teku zuwa teku, daga dutsezuwa dutse.

13. Duniya kuwa za ta zama kufai,Saboda mazaunan da suke cikinta,Saboda hakkin ayyukansu.

14. Sai ka yi kiwon mutanenka dasandanka,Wato garken mallakarka,Wanda yake zaune shi kaɗai a kurmiA tsakiyar ƙasa mai albarka.Bari su yi kiwo cikin Bashan daGileyadKamar a kwanakin dā.

15. “Zan nuna muku abubuwa masubanmamaki,Kamar a kwanakin da kuka fitoƙasar Masar.”

16. Al'umman duniya za su gani,Su kuwa ji kunyar ƙarfinsu duka.Za su sa hannuwansu a baka,Kunnuwansu za su kurmance.

17. Za su lashi ƙura kamar maciji daabubuwa masu rarrafe,Za su fito da rawar jiki daga wurinmaɓuyarsu,Da tsoro za su juyo wurin UbangijiAllahnmu,Za su ji tsoronka.

18. Akwai wani Allah kamarka, mai yafemugunta,Mai kawar da laifin ringingādonsa?Ba ya riƙon fushi har abada, gamashi mai alheri ne.

Karanta cikakken babi Mika 7