Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mika 7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Lalacewar Isra'ila

1. Tawa ta ƙare, gama na zamakamar lokacin da aka gamatattara amfanin gona,Kamar lokacin da aka gama kalar'ya'yan inabi,Ba nonon inabi da za a tsinka, a ci,Ba kuma 'ya'yan ɓaure da sukaharba wanda raina yake so.

2. Mutanen kirki sun ƙare a duniya,Ba nagarta a cikin mutane.Dukansu suna kwanto don su zub dajini.Kowa yana farautar ɗan'uwansa datarko.

3. Sun himmantu su aikata abin da yakemugu da hannuwansu.Sarki da alƙali suna nema a ba suhanci,Babban mutum kuma yana faɗar sonzuciyarsa,Da haka sukan karkatar da zance.

4. Mutumin kirkinsu kamar ƙaya yake,Mai gaskiyarsu kuwa kamar shingenƙaya yake.Ranar da kuka sa mai tsaro,A ran nan za a aukar muku dahukunci.Yanzu ruɗewarku ta zo,

5. Kada ka dogara ga maƙwabcinka,Kada kuma ka amince da abokinka.Ka kuma kame bakinka dagamatarkaWadda take kwance tare da kai.

6. Gama ɗa yana raina mahaifi,'Ya kuma tana tayar wamahaifiyarta,Matar ɗa kuma tana gāba dasurukarta,Mutanen gidan mutum su nemaƙiyansa.

Ubangiji Zai Kawo Haske da Ceto

7. Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji,Zan jira ceton Allahna,Allahna zai ji ni.

8. Ya maƙiyina, kada ka yi murna akaina,Gama sa'ad da na fāɗi, zan tashikuma.Sa'ad da na zauna cikin duhu,Ubangiji zai haskaka ni.

9. Zan ɗauka fushin Ubangiji ne,Gama na yi masa zunubi,Sai lokacin da ya ji da'awata,Har ya yanke mini shari'a.Zai kawo ni zuwa wurin haske,Zan kuwa ga cetonsa.

10. Sa'an nan maƙiyina wanda suke ce mini,“Ina Ubangiji Allahnka?”Zai gani, ya kuma ji kunya.Idanuna za su gan shi lokacin da akatattake shiKamar taɓo a titi.

11. Za a faɗaɗa iyakarkaA ranar da za a gina garunka.

12. A waccan rana mutane za su zowurinka,Daga Assuriya har zuwa Masar,Daga Masar zuwa Kogin Yufiretis,Daga teku zuwa teku, daga dutsezuwa dutse.

13. Duniya kuwa za ta zama kufai,Saboda mazaunan da suke cikinta,Saboda hakkin ayyukansu.

Juyayin Ubangiji a kan Isra'ila

14. Sai ka yi kiwon mutanenka dasandanka,Wato garken mallakarka,Wanda yake zaune shi kaɗai a kurmiA tsakiyar ƙasa mai albarka.Bari su yi kiwo cikin Bashan daGileyadKamar a kwanakin dā.

Labarin Fāɗuwar Nineba

15. “Zan nuna muku abubuwa masubanmamaki,Kamar a kwanakin da kuka fitoƙasar Masar.”

16. Al'umman duniya za su gani,Su kuwa ji kunyar ƙarfinsu duka.Za su sa hannuwansu a baka,Kunnuwansu za su kurmance.

17. Za su lashi ƙura kamar maciji daabubuwa masu rarrafe,Za su fito da rawar jiki daga wurinmaɓuyarsu,Da tsoro za su juyo wurin UbangijiAllahnmu,Za su ji tsoronka.

18. Akwai wani Allah kamarka, mai yafemugunta,Mai kawar da laifin ringingādonsa?Ba ya riƙon fushi har abada, gamashi mai alheri ne.

19. Zai sāke jin juyayinmu,Ya tattake muguntarmu a ƙarƙashinƙafafunsa.Za ka jefar da zunubanmu a cikinzurfin teku.

20. Za ka nuna wa Yakubu aminci,Ga Ibrahim kuma madawwamiyarƙauna,Kamar yadda ka rantse wakakanninmuTun a zamanin dā.