Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mak 2:8-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ubangiji ya yi niyyaYa mai da garun Sihiyona kufai,Ya auna ta da igiyar awo,Bai janye dantsensa daga hallaka ta ba.Ya sa kagara da garu su zozaye, su lalace tare.

9. Ƙofofinta sun nutse ƙasa,Ya lalatar, ya kakkarya ƙyamarenta,An kai sarkinta da mahukuntanta cikin al'ummai,Inda ba a bin dokokin annabawanta,Ba su kuma samun wahayi daga wurin Ubangiji.

10. Dattawan Sihiyona suna zaune a ƙasa shiru,Sun yi hurwa, suna saye da tufafin makoki.'Yan matan Urushalima kuma sun sunkuyar da kansu ƙasa.

11. Idanuna sun dushe saboda kuka,Raina yana cikin damuwa.Zuciyata ta karai saboda halakar mutanena,Gama 'yan yara da masu shan mamaSun suma a titunan birnin.

12. Suna yi wa uwayensu kuka, suna cewa,“Ina abinci da ruwan inabi?”Suna suma kamar mutanen da aka yi wa rauniA titunan birnin,Suna mutuwa a ƙirjin uwayensu.

Karanta cikakken babi Mak 2