Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mak 1:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Sihiyona tana miƙa hannuwanta,Amma ba wanda zai ta'azantar da ita.Gama Ubangiji ya umarci maƙwabtan Yakubu su zama maƙiyansa.Urushalima kuma ta zama ƙazantacciya a tsakaninsu.

18. “Abin da Ubangiji ya yi daidai ne,Gama ni na ƙi bin maganarsa,Ku ji, ya ku jama'a duka,Ku dubi wahalata,'Yan matana da samarina,An kai su bauta!

19. “Na kira masoyana, amma suka yaudare ni,Firistocina da dattawana a cikin birni sun hallakaSaboda neman abincin da za su ci su rayu.

20. “Ka duba, ya Ubangiji, ina shan wahala,Raina yana cikin damuwa,Zuciyata tana makyarkyata saboda tayarwata.A titi takobi yana karkashewa,A gida kuma ga mutuwa.

Karanta cikakken babi Mak 1